Hukumar zabe ta kasa mai zaman kanta, wato INEC, ta tabbatar da cewa ta zabi ranar 9 ga watan Maris matsayin ranar sake gudanar da zaben shugaban kasa a wasu wuraren da aka samu matsala a ranar Asabar, 23 ga watan Febrairu, 2019.
Kwamishanan labarai na hukumar INEC, Festus Okoye, ya bayyana cewa za’a gudanar da zaben ne tare da zaben gwamnoni da majalisar dokokin tarayya.
Okoye ya ce an yanke wannan shawara ne bayan ganawar hukumar da wakilan INEC dake jihohin tarayya a ranar Alhamis, 28 ga watan Febrairu, 2019.
INEC ta yi watsi da zaben wasu wurare sakamakon rikice-rikice wanda ya hana hukumar aika kayan zabe da ma’aikata wajen domin kare rayukansu.
Wadannan wurare sun kunshi kananan hukumomi biyu a jihar Ribas,da wasu a jihar Legas da jihar Anambara.
Jawabin yace: ” Saboda haka, hukumar ta yanke shawara cewa za’a gudanar da zaben a dukkan wuraren da ba’a samu damar gudanar da zabe ba a ranan Asabar, 9 ga watan Maris tare da zaben gwamnoni da yan majalisun dokokin jiha,”.
Idan Za ku tuna cewa rikice-rikice a unguwar Okota dake jihar Legas ya sanadiyyar INEC tayi watsi da sakamakon zaben wajen, kana kashe-kashe da aka yi a jihar Ribas inda akalla mutane 20 suka rasa rayukansu ranar zabe.