Za a samu tsauri a wa’adin mulkina na biyu – Buhari

Muhammadu Buhari

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana cewa wa’adin mulkinsa na biyu zai kasance mai tsauri sakamakon irin alkawuran da ya dauka zai cikawa ‘yan Najeriya na habaka tattalin arziki da kuma yaki da cin hanci da rashawa da tabbatar da tsaro.

Shugaban ya bayyana haka ne a wata tattaunawa ta musamman da ya yi da ministocinsa a lokacin da suka kawo masa ziyara a fadar shugaban kasar domin taya shi murnar lashe zaben kasar.

Shugaban ya ce, ”Ina ganin shekaru hudu nawa na karshe a kan mulki za su zama tsaurara saboda ina tunanin mutane na da mantuwa, wannan ne ya sa duk wurin da naje ina kara tuni da cewa yakin neman zabenmu muna yin sa ne kan abubuwa uku.”

Shugaban ya bayyana tabbatar da tsaro a matsayin abu na farko inda ya ce sai an samar da tsaro kafin a iya mulkar kasa yadda ya kamata.

Ya kuma bayyana tattalin arziki a matsayin abu na biyu inda ya ce ”marasa aikin yi a Najeriya su ne babbar matsalar kasar, ya ce sama da kashi 60 cikin 100 na ‘yan kasar matasa ne wanda hakan na nufin ‘yan kasa da shekara 35, dole ne a samar masu da aikin yi.”

Shugaban ya kara da cewa ”na ga alamun cewa Allah ya amsa addu’ar mu domin damina biyu da suka gabata Allah ya sa masu albarka wanda kafin hakan ne muka yi zurfin tunani muka sa ma’aikatar ayyukan gona da raya karkara tare da hadin gwiwar babban bankin Najeriya suka bayar da bashi ga manoma domin ganin cewa masu jini a jika da suke da gonaki sun koma gona.”

Shugaban wanda ya kuma tattauna a kan fitarsa yakin neman zabe ya ce hakan ya baiwa ‘yan adawa kunya da suke cewa bai da kuzarin mulkar Najeriya, amma ya ce wannan alama ce da ta nuna cewa ya shirya tsaf domin mulkar Najeriya na shekaru hudu masu zuwa.

A ranar Laraba ne dai hukumar zabe a Najeriyar ta bayyana Shugaban Kasar Muhammadu Buhari a matsayin wanda ya yi nasara a zaben da aka gudanar a ranar Asabar bayan ya fafata da Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP.

Sai dai dan takarar PDP Atiku ya yi watsi da sakamakon zaben da hukumar zaben ta bayyana inda yake zargin an tafka kura-kurai wajen gudanar da zaben.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...