Za a kafa sabuwar gwamnati a Sudan ta kudu | BBC Hausa

Shugaban Sudan ta Kudu ta Salva Kiir
Image caption

Gamayyar kungiyoyin farar hula a Sudan ta Kudu, sun yi kira ga kwamitin tsaro na MDD ya yi kokarin kafa sharuddai da dokokin da za su kare kasar daga sake fadawa yaki.

Wannan na kunshe ne a wata sanarwa da kungiyoyin suka fitar bayan saba lokacin da aka cimma yarjejeniyar zaman lafiya da ya kamata a ce ta fara aiki a ranar 12 ga wannan watan.

Kungiyoyin rajin kare hakkin jama’a 200 ne suka tattaunawa da fitar da abubuwa guda 5 da suke fatan ganin kwamitin tsaro na MDD ya yi dan sake gina sabuwar sudan ta kudu wadda yakin basasa na shekara 5 ya daidaita.

Geoffrey Duke shi ne jagoran wannan tafiya, ya kuma ce abu na farko su na bukatar sabon kwamitin wanzar da zaman lafiya tsakanin bangarortin da ke rikici da juna da kuma suka rattaba hannu kan yarjejeniyar su yi kokarin samar da gwamnatin hadaka daga nan zuwa 12 ga watan Nuwamba mai zuwa.

Sannan kwamitin tsaro na MDD ya sauke hakkin da ya rataya akan sa na kare farar hular Sudan ta Kudu, da kuma daukar irin matakin da aka dauka a baya.

Sai kuma kasashe makofta su tabbatar ba a shiga ko fota da makamai daga kasar zuwa cikinsu ba, da tabbatzr da ba a sace ma’adinai da dukiyar kasa ta hanyar tsallaka iyakokinsu ba.

Haka kuma kungiyar tarayyar afirka ta samar da kotun hukunta manyan laifuka a Sudan ta Kudun, kamar yadda aka gabatar da bykatar hakan a lokacin tattunawar sulhu.

A karshe masu zuba jari na kasashen waje su dawo kasar dan farfado da wannan bangaren ba wai zuba jari kadai ba har da ba da gudummawar farfado da dimukradiyyar kasar. Inda za su zuba ido kan shugabannin kasar yadda da sun karya wata doka daga cikin dokokin da aka shardanta za a hukuntasu.

A watan Satumbar bara ne dai aka yi zaman sulhunta shugaba Salva Kiir da tsohon mataimakinsa kuma madugun ‘yan tawaye Riek Machar da ya ke gudun hijira bisa radin kan sa, amma daga wancan lokaci zuwa yanzu ba bu wani abun azo a gani da aka cimma da nufin ci gaban Sudan ta kudun.

Mr Duke, ya ce wadanda alhakin komai ya rataya a kansu su na da watanni 6 nan gaba da za su yi aiki tare dan kawo karshen halin da ‘yan Sudan ta Kudun suke ciki.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...