Yau take Ranar Dimokradiyya a Najeriya

Moshood Abiola

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

A yau Laraba ne Shugaban Muhammadu Buhari ke kaddamar da ranar dimokradiyya a karon farko, bayan mayar da ita zuwa bikin 12 ga watan Yuni maimakon 29 ga watan Mayu kamar yadda aka saba a baya.

Bikin ranar 12 ga watan Yuni, na tunawa ne da zaben shugaban Najeriya na 1993, wanda akasarin mutane suka yi imani cewa sanannen dan siyasar kasar marigayi Cif MKO Abiola ne ya yi nasarar ci, kafin gwamnatin mulkin soja ta lokacin Janar Ibrahim Badamasi Babangida, ta soke zaben.

Kafofin labaran Najeriya sun ruwaito cewa, Shugaba Buhari ya sanya hannu a kan kudurin dokar da ya mayar da 29 ga Mayu ranar mika mulki, ita kuma 12 ga Yuni ta kasance ranar hutu don bikin dimokradiyya a kasar.

Sai dai kuma a wani bangaren, wasu tsoffin ‘ya’yan tsohuwar jam’iyyar NRC a jamhuriya ta uku, sun kalubalanci matakin mayar da 12 ga Yuni a matsayin ranar dimokradiyya.

‘Ya’yan tsohuwar jam’iyyar NRC din sun ce ba sa goyon bayan wannan mataki, don a cewarsu dan takararsu Alhaji Bashir Tofa ne ya ci zaben, amma ba Moshood Abiola na SDP ba.

Honorabul Mas’ud Jibril Doguwa shi ne tsohon sakataren jam’iyyar NRC a jihar Kano kuma ya shaida wa BBC cewa ”duk wani dan NRC a Najeriya kwace aka yi masa, ba mu yarda a ce an mayar da wannan ranar dimokradiyya ba.”

Sai dai tun bayan da kasar ta koma turbar dimokradiyya a shekarar 1999, wani babban kalubale da take fuskanta shi ne na tabarbarewar sha’anin tsaro wanda kawo yanzu tana kasa tana dabo kan batun shawo kansa.

Sa’annan kuma cin hanci da rashawa na daya daga cikin abubuwan da suka yi wa kasar katutu inda har shugaban kasar ya ayyana shi a matsayin manyan abubuwan da zai yi yaki da su.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ćłan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...