Yau Ne Sabuwar Ranar Dimokaradiyya A Najeriya

An gayyato shugabannin kasashen duniya daban-daban da jakadun ‘kasa da ‘kasa domin taya Shugaba Buhari murna.

A lokacin da shugaba Muhammadu Buhari yake yakin neman zaben wa’adi na biyu ya kara nanata cewa “Alkiblar wa’adi na biyu kamar na farko ne, shine yaki da cin ranci da rashawa, samar da tsaro da farfado da tattalin arziki”

Wannan bayanin dai shine yadan kara bada haske da nuna alkibla akan bayanan da gwamatin shugaba Muhammadu Buhari za ta yi ranar 12 ga watan Yunin shekarar 2019.

Inda ake sa ran zai fayyace dallah-dallah canje canje ko garanbawul da wannan fannonin zasu samu domin tabbatar da yaki da cin ranci da rashawa da matsalar tsaro, matsalar da al’umma da dama suke gani cewa tana ci gaba da tabarbarewa, duk da makudan kudade da gwamnatin ke kashewa wajen inganta tsaro a Najeriya.

Wannan bikin da za a yi yana da muhimmanci domin gwamnati zata kaddamar da 12 ga watan Yuni ko wacce shekara a matsayin ranar dimokaradiyyar Najeriya.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...