Yara da dama sun makale a ginin bene da ya ruguzo a Lagos

Wani ginin bene mai hawa uku da ke yankin Itaa-Faaji a jihar Lagos ya rushe sannan ya danne yara yan makaranta da dama.

Wani shedan gani da ido ya fadawa jaridar The Cable cewa lamarin yafaru ne da misalin karfe goma na ranar Laraba. Daya daga cikin hawan benen ana amfani da shi ne a matsayin makaranta kuma yara dalibai na tsaka da karatu lokacin da ginin ya rufta.

Jami’an hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Lagos da sauran ma’aikatan ceto na can suna aikin ceto yaran dama sauran mutanen da suka makale.

An garzaya da wasu daga cikin yaran da aka samu nasarar zakulo su daga cikin baraguzan ginin.

Faduwar gini irin haka abune da ya zama ruwan dare a Najeriya kuma da alama hukumomi sun gaza daukar mataki da zai kai ga shawo kan faruwar lamarin.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...