Kungiyar Barcelona za ta karbi bakuncin Lyon a wasa na biyu zagaye na biyu a gasar cin kofin Zakarun Turai ta Champions League da za su kara ranar Laraba a Camp Nou.
Kungiyoyin biyu sun fafata a wasan farko a gasar ranar 19 ga watan Fabrairu a Faransa inda suka tashi wasa babu ci.
Tuni kocin na Barcelona, Ernesto Valverde ya bayyana ‘yan wasa 20 da za su buga masa karawar da za suyi a Spaniya
‘Yan wasa 20 da za su fuskanci Lyon:
Ter Stegen da N. Semedo da Piqué da I. Rakitic da Sergio da Coutinho da Arthur da Suárez da kuma Lionel Messi.
Sauran sun hada da Dembélé da Cillessen da Malcom da Lenglet da Murillo da Jordi Alba da Prince da Roberto da Vidal da Umtiti da kuma Aleñá.