‘Yan ta’adda sun ‘tayar da gari’ a Jihar Zamfara

zamfara taswira

Rahotanni daga Jiihar Zamfara na cewa wasu ‘yan bindiga sun farma wani kauye inda suka kashe mutane da dama a karamar hukumar Shinkafi.

An kai harin ne a kauyen Kware a tsakiyar dare a ranar Lahadi, kuma baya ga kashe mutane ‘yan bindigar sun kone gidajen mutane da dama, kamar yadda wani mazauni kauyen wanda shi ma ya ce an kone gidansa ya tabbatarwa da BBC.

Ya ce sun kirga gawawwakin mutane kimanin 40 da ‘yan bindigar suka kashe.

Ya kuma ce sun gudu zuwa daji, yayin da mutanen kauyen da dama suka yi gudun hijira zuwa makwabta.

“Zuwa yanzu za mu iya cewa sun kwace ikon garin,” in ji shi.

Sai dai zuwa yanzu rundunar ‘yan sandan jihar ta Zamfara ba ta fitar da sanarwa ba game da al’amarin.

Wannan harin na zuwa ne bayan ‘yan bindiga sun kashe mutane da dama a wani hari da suka kai yankin a ranar Alhamis.

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Image caption

An shafe shekaru Zamafara na fama da matsalar ‘yan bindiga

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...