‘Yan Najeriya sun yi zarra a gasar karatun Kur’ni a Saudiyya | BBC Hausa

Wadanda sukja yi nasara a gasar karatun Kur'ani ta 2019 a Saudiyya

Hakkin mallakar hoto
@makkahregion

Image caption

‘Yan Najeriya uku ne suka yi zarra a gasar ta bana

Wasu ‘yan Najeriya uku Abubakar Muhammad da Amir Yunus Goro da kuma Abdulganiyyi Amin sun yi nasarar lashe kyautuka a gasar karatun Al Kur’ani ta 2019 a kasar Saudiyya a matakai daba-daban.

Gwani Idris Abubakar Muhammad daga jihar Borno ta Najeriya, ya zo na daya ne a ajin farko na izu sittin ba tare da tafsiri ba.

Wannan nasara da ya samu ta ba shi damar lashe kyautar riyal na Saudiyya 120,000 – kimanin kusan naira milyan ₦12,000,000.

Sai Amir Yunus, wanda shi kuma ya zo na uku a ajin farko na izu sittin da tafsiri, inda ya samu kyautar riyal 150.000 – sama da naira miliyan ₦14,000,000.

Abdulganiyyi Amin shi ne na ukun, wanda ya zo na uku shi ma a aji na biyu na izu sittin ba tare da tafsiri ba.

Shi kuma ya samu kyautar riyal 40,000 – kusan naira miliyan ₦4,000,000.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...