[ad_1]
Aƙalla ƙananan yara 33 ne suka mutu a sansanin yan gudun hijira dake Bama a jihar Borno sakamakon ƙarancin abinci kungiyar likitoci ta Médecins Sans Frontières (MSF) ce ta bayyana haka.
Ƙungiyar ta bayyana haka cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Juma’a.
Garin Bama na daya daga cikin garuruwan da rikicin kungiyar ta Boko Haram ya yi wa muguwar barna da kuma sauran garuruwa dake yankin arewa maso gabas.
“Karancin isasshen taimako, da ya haɗa da makwanci da kiwon lafiya na yin mummunan illa akan kananan yara dake isa garin,”MSF ta bayyana a cikin sanarwar.
“Tun daga watan Afirilun shekarar 2018 sama da mutane 10000 ne suka isa sansanin yan gudun hijira na makarantar sakandaren kimiyya inda muhalli da kuma kula da lafiya basa tafiya kafada da kafada da yawan mutanen da suke karuwa.”
Rahoton ya kara da cewa sama da mutane 6000 ne dake sansanin ke kwana a filin Allah ba tare da kariya daga zafin rana, ruwan sama da kuma sauro.
[ad_2]