Yan gudun hijira na cikin mawuyacin hali a garin Bama inda ƙananan yara 33 suka mutu

[ad_1]








Aƙalla ƙananan yara 33 ne suka mutu a sansanin yan gudun hijira dake Bama a jihar Borno sakamakon ƙarancin abinci kungiyar likitoci ta Médecins Sans Frontières (MSF) ce ta bayyana haka.

Ƙungiyar ta bayyana haka cikin wata sanarwa da ta fitar ranar Juma’a.

Garin Bama na daya daga cikin garuruwan da rikicin kungiyar ta Boko Haram ya yi wa muguwar barna da kuma sauran garuruwa dake yankin arewa maso gabas.

“Karancin isasshen taimako, da ya haɗa da makwanci da kiwon lafiya na yin mummunan illa akan kananan yara dake isa garin,”MSF ta bayyana a cikin sanarwar.

“Tun daga watan Afirilun shekarar 2018 sama da mutane 10000 ne suka isa sansanin yan gudun hijira na makarantar sakandaren kimiyya inda muhalli da kuma kula da lafiya basa tafiya kafada da kafada da yawan mutanen da suke karuwa.”

Rahoton ya kara da cewa sama da mutane 6000 ne dake sansanin ke kwana a filin Allah ba tare da kariya daga zafin rana, ruwan sama da kuma sauro.




[ad_2]

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miƙata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaƙi da yiwa tattalin arzikin ƙasa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar ƴan sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...