Kusan ‘yan cirani 100 da ke kan wani jirgin ruwa na jin kai wanda ya makale a tsibirin Lampedusa sun bar tsibirin na Italiya, bayan wani mai shigar da kara ya umarci jirgin ruwan da ya bar tsibirin.
Lokacin da jirgin ya isa tsibirin dai, mutane sun yi musu maraba a yayin da suka dinga sowar “sannu da zuwa” musamman ma ga ‘yan ciranin Afirka.
Mai shigar da kara, Luigi Patronaggio ya umarci da a kwace jirgin wanda mallakin wata kungiyar agaji mai suna Open Arms ne.
Kungiyar ta ce ‘yan ci ranin za su iya fara samun kulawar likitoci, duk da gwamnatin Italiya ta jima tana hana su shiga kasar.
Kafin mai shigar da karar ya yanke hukuncinsa, Sipaniya wadda ita ce gida ga kungiyar ta Open Arms ta aika wani jirgin ruwa zuwa Lampedusa domin ya dauko ‘yan ci ranin.