‘Yan Bindinga Sun Hallaka Mutane 8 A Kan Iyakar Nasarawa Da Benue

Wassu ‘yan bindiga da ba a san ko su wanene ba sun kai hari a kauyen Ebete dake yankin Agatu a jahar Binuwai, suka hallaka mutane takwas wassu hudu kuma suna kwance a asibiti ana musu jinya.

Kauyen na Ebete dai na gabar kogin Binuwai ne dake kan iyakar jihar da ta Nasarawa.

Wani mai suna Collins Edache, wanda dan uwa ne ga iyalin da aka kashe, ya ce lamarin ya auku ne da missalin karfe sha biyu saura kwata na daren jiya laraba.

Mai magana da yawun hukumar ‘yan sandan jihar Binuwai, DSP Sewuese Anene ta shaida cewa lallai lamarin ya auku, sai dai a cewarta kwamishinan ‘yan sandan jihar ne zai iya yin karin bayani.

Rahotanni dai sun nuna cewa mutane goma sha shida ne suka rasa ransu a harin na jiya laraba.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...