‘Yan bindiga sun kai hari a jihar Jigawa

Getty Images

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Rundunar ‘yan sandan Najeriya a jihar Jigawa ta tabbatar cewa barayi sun halaka mutum daya tare da jikkata wasu mutane, a wani hari da barayin suka kai a garin Maidawa da ke jihar.

Bayanai sun ce maharan sun shiga kauyen ne kan babura, sannan suka je gidan wani attajiri a kauyen suka karbi kudi, suka kuma harbe shi tare da wasu mutanen garin.

Cikin wandanda aka harba har da wasu yara uku kamar yadda aka bayyana.

Duk da cewa ‘yan sanda sun bayyana cewa mutum daya aka kashe, amma mazauna garin na ikirarin kashe mutane da dama a harin da barayin suka kai.

An bayyana cewa barayin sun kai kusan mintuna arba’in suna cin karensu ba babbaka a cikin garin na Maidawa.

Mazauna kauyen sun koka bisa ga faruwar wannan lamarin inda suke ganin kamar irin abubuwan da ke faruwa a wasu wurare sun fara isowa yankin su.

Wasu kuma mazauna garin sun shaida cewa da wayansu ba su taba ganin an kawo hari da bindigogi ba a garin.

Wannan harin da aka kai a Jigawa na zuwa ne a daidai lokacin da matsalar garkuwa da mutane da kuma fashi da makami ke kara kamari musamman a jihohin arewa maso yammacin Najeriya.

Sai dai gwamnatin kasar ta bayyana cewa tana iya bakin kokarinta wajen shawo kan matsalolin.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...