Wani sabon rahoto da aka fitar dauke da cewa Jarirai 5 ne ke mutuwa sanadiyyar yaki, kafin soja guda ya mutu.
Rahoton da kungiyar Save the Children ta fitar, ta ce shekaru biyar da suka gabata, jarirai dubu dari biyar ne ke mutuwa a kowacce rana, sanadiyyar yaki.
Wasu lokutan kuma 300 ko dai sanadiyyar yunwa da rashin abinci mai gina jiki, ko cututtuka kamar amai da gudawa da rashin kulawar likita da magani.
Kasashen da lamarin ya fi munana sun hada da Yemen da Syria da Afghanistan, da Jamhuriyyar Dimukradiyyar Congo.
Save the Children ta ce idan za a hada da yara ‘yan shekara biyar da ke mutuwa, adadin ka ya kai waDubu dari tara.
Haka kuma ba a sanya yaran da suka mutu a lokacin da ake gwabza yakin ba, ko dai ta harbin bindiga, ko tashin bam ko rikitowar gine-gine.