Wasu ‘yan siyasa a Zamfara sun nuna jin dadinsu game da dage zabe

Wasu ‘yan jam’iyyar APC a jihar Zamfara, musamman magoya bayan bangaren ‘yan takarar gwamnan jihar Abdul’aziz Yari sun nuna farin cikinsu game da dage zaben Najeriya da aka yi.

Har ya zuwa daren jiya dai jam’iyyar ta APC a jihar bata san makomarta a zaben ba, sakamakon matsayar hukumar zabe na cewa jam’iyyar a jihar ba ta da ‘yan takara a zaben na bana, kuma bata bada wata sanarwar warware matsayar ba, kwatsam sai ga sanarwar dage zabe.

Sai dai a bangare daya, duk da yake ‘yan jam’iyyar adawa ta PDP a jihar da suke ta murnar matsayar hukumar zaben basu ji dadin dage zaben ba, suna ganin ba wani tasiri da hakan zai haifar.

To ko wannan ka iya kasancewa dama ga jam’iyyar APC a jihar ta samun shigar ‘yan takarar a zaben? Kakakin gwamnan jihar Zamfara, Ibrahim Dosara ya ce yana fatan hakan.

Da tsakiyar dare ne dai hukumar zaben Nigeria ta bada sanarwar dage babban zaben kasar da mako daya, lamarin da ya sa al’amuran yau da kullum suka dawo tamkar yadda aka saba a babban birnin jihar.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...