Wasu ‘yan siyasa a Zamfara sun nuna jin dadinsu game da dage zabe

Wasu ‘yan jam’iyyar APC a jihar Zamfara, musamman magoya bayan bangaren ‘yan takarar gwamnan jihar Abdul’aziz Yari sun nuna farin cikinsu game da dage zaben Najeriya da aka yi.

Har ya zuwa daren jiya dai jam’iyyar ta APC a jihar bata san makomarta a zaben ba, sakamakon matsayar hukumar zabe na cewa jam’iyyar a jihar ba ta da ‘yan takara a zaben na bana, kuma bata bada wata sanarwar warware matsayar ba, kwatsam sai ga sanarwar dage zabe.

Sai dai a bangare daya, duk da yake ‘yan jam’iyyar adawa ta PDP a jihar da suke ta murnar matsayar hukumar zaben basu ji dadin dage zaben ba, suna ganin ba wani tasiri da hakan zai haifar.

To ko wannan ka iya kasancewa dama ga jam’iyyar APC a jihar ta samun shigar ‘yan takarar a zaben? Kakakin gwamnan jihar Zamfara, Ibrahim Dosara ya ce yana fatan hakan.

Da tsakiyar dare ne dai hukumar zaben Nigeria ta bada sanarwar dage babban zaben kasar da mako daya, lamarin da ya sa al’amuran yau da kullum suka dawo tamkar yadda aka saba a babban birnin jihar.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...