Tottenham ta ci gaba da bude wuta a Firimiya

Tottenham

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Tottenham ta casa Leicester City da ci 3-1 a wasan mako na 26 a gasar cin kofin Premier da suka fafata a ranar Lahadi a Wembley.

Tottenham ta fara cin kwallo ta hannun Davinson Sanchez a minti na 33 da fara wasa, Leicester ta samu damar farkewa a bugun fenariti, amma Jamier Vardy ya barar.

Bayan da aka koma daga hutu ne Eriksen ya kara na biyu daga baya Vardy na Leicester ya zare daya, sai dai daf da za a tashi daga fafatawar Son Heung-Mi ya ci na uku.

Da wannan sakamakon Tottenham tana nan a mataki na uku da maki 60, maki biyar tsakaninta da Liverpool ta daya a teburi, sannan maki biyu tsakaninta da City wadda za ta karbi bakuncin Chelsea.

A ranar Asabar Liverpool ta doke Bournemouth da ci 3-0 a karawar mako na 26 a gasar ta Premier da suka kara a Anfield.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...