Talauci Zai Ƙaru A Najeriya Nan Da Shekarar 2027—Bankin Duniya

Bankin Duniya ya yi hasashen cewa Najeriya za ta fuskanci karuwar talauci da kaso 3.6 cikin ɗari nan da shekarar 2027, duk da wasu ƙananan cigaba da aka samu a sashen da ba na mai ba a karshen 2024.

Wannan na cikin rahoton Africa’s Pulse da aka fitar yayin taron bazara da Bankin Duniya da Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ke gudanarwa a Washington, D.C.

Rahoton ya nuna cewa matsalolin da suka shafi dogaro da albarkatu da rashin kwanciyar hankali na cikin gida za su hana rage yawan talakawa a Najeriya da sauran kasashe masu irin wannan yanayin.

“Talauci a kasashe masu albarkatu kuma masu fama da rikici — ciki har da manyan kasashe kamar Najeriya da Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Kongo — ana sa ran zai karu da kaso 3.6 cikin dari daga shekarar 2022 zuwa 2027,” in ji rahoton.

Rahoton ya kara da cewa Sub-Saharan Africa na da mafi girman adadin masu fama da talauci a duniya.

A shekarar 2024, kashi 80 cikin ɗari na mutanen duniya miliyan 695 da ke cikin talauci mai tsanani sun fito daga wannan yanki.

Cikin kasashen yankin, rahoton ya bayyana cewa rabin talakawan da suka kai miliyan 560 suna zaune a ƙasashe huɗu ne kawai.

More from this stream

Recomended