Sudan: Malaman jami’a sun fara zanga-zanga

Men in a pickup truck

Hakkin mallakar hoto
Protester

Jami’an tsaro a Sudan suna tsare da wasu malaman jami’a da suka fito zanga-zanga a Khartoum, babban birnin kasar.

Likitoci da dama sun fito suna zanga-zanga a asibitoci inda suke kira da shugaban kasar ya sauka daga mukaminsa, kuma tun watan Disambar bara jama’ar kasar ke karawa da jami’an tsaro.

Kungiyar Human Rights Watch mai fafutukar kare hakkin bil Adama ta ce jami’an tsaro sun kashe akalla mutum 50.

Ba kamar yadda aka saba gani a wasu sassa na nahiyar Afirka ba – inda yawancin masu fita zanga-zangar adawa da gwamnati kan kasance matasa marasa aikin yi ne.

Hakkin mallakar hoto
Reuters

Image caption

Omar al-Bashir ya mulki Sudan tun 1989

Amma a Sudan likitoci maza da mata da malaman makaranta da sauran ma’aikata ne ke fuskantar harsasai da hayaki mai sa hawaye da kuma kulakan ‘yan sandan gwamnatin Shugaba Omar al Bashir.

‘Yan sa’o’i kadan da suka gabata an kame wasu malaman jami’a a birnin Khartoum.

An kuma gabatar da wasu jerin zanga-zanga a asibitoci goma cikin babban birnin kasar – an kuma bukaci Shugaba Omar al Bashir ya sauka daga mukaminsa.

Mako biyu da ya gabata gwamnatin Sudan ta ce za ta saki dukkan wadanda ta damke sakamakon zanga-zangar da aka shafe fiye da wata biyu ana yi a fadin kasar.

Amma yawancin wadanda ke tsaren ba su sami ‘yancinsu ba.

Masu rajin kare hakkin dan Adam a Sudan na fargabar cewa gwamnati na iya kama su domin gwamnatin kasar na tsare da mutane masu yawa a wurare na sirri.

Suna kuma tsorn jami’an tsaron na iya gallaza masu azaba.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...