Solomon Dalung Ya Bayyana Abin Da Ke Janyo Yawan Sauya Sheƙa Zuwa Jam’iyyar APC

Tsohon Ministan Matasa da Wasanni, Solomon Dalung, ya ce bukatar samun kariya daga tuhumar rashawa ce babbar dalilin da ke jawo yawaitar sauya sheka zuwa jam’iyyar APC mai mulki.

Dalung ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi a shirin The Morning Brief na Channels Television a ranar Talata, sa’o’i kadan bayan wasu fitattun ’yan siyasa sun sauya sheka zuwa APC.

A cewar rahotanni, Gwamnan Jihar Delta, Sheriff Oborevwori, da wanda ya gabace shi, Ifeanyi Okowa, sun tabbatar da sauya shekarsu zuwa APC.

Duk da cewa Oborevwori ya bayyana cewa matakin da suka dauka yana da alaka da ci gaban jiharsu mai arzikin man fetur, Dalung bai yarda da wannan hujja ba.

A cewarsa: “Wannan guguwar sauya sheka da ’yan siyasa ke yi a halin yanzu wata hanya ce ta neman tsira, kariya daga bincike ko kuma kaucewa gurfanarwa. Ga duk wanda ya fahimci siyasar Najeriya sosai, ba za a dauki hakan da muhimmanci ba.”

Ya kara da cewa kamata ya yi masu jefa kuri’a su kasance masu yanke hukunci kan ko dan siyasa ya cancanci sauya sheka ko a’a.

More from this stream

Recomended