Sojoji sun yi luguden wuta wa ƴan ta’adda a Kaduna

Rundunar sojin sama ta Najeriya NAF ta ce ta kashe ‘yan ta’adda da dama a Tsauni Doka da ke karamar hukumar Igabi a jihar Kaduna.

Daraktan hulda da jama’a da yada labarai na NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

Ya ce rundunar ta NAF na Operation Whirl Punch ce ta kai harin.

Mista Gabkwet ya ce an kai harin ne bayan wasu sahihin bayanan sirri sun nuna akwai wani shugaban ‘yan ta’adda da aka fi sani da Boderi da sojojinsa a Tsauni Doka.

Ya ce an kai hare-haren ta sama a wurin da sanyin safiyar ranar 16 ga watan Nuwamba, wanda ya haifar da mummunan sakamako ga ‘yan ta’addar.

More News

Kotu ta sauke kakakin majalisar Nasarawa

Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke zamanta a Abuja ta kori kakakin majalisar dokokin jihar Nasarawa, Rt. Hon. Ibrahim Balarabe Abdullahi dan jam’iyyar...

Masu cin gajiyar shirin Npower na kokawa game da rashin biyansu

Wasu masu cin gajiyar shirin gwamnatin tarayya na N-Power a ranar Litinin sun koka kan yadda ake ci gaba da biyan su alawus-alawus din...

Tinubu ya sake naɗa Mele Kyari a matsayin shugaban NNPCL

Shugaba Bola Tinubu ya sake nada Malam Mele Kyari a matsayin babban jami’in gudanarwa na kamfanin man fetur na kasa (NNPCL). An bayyana hakan ne...

Ba baƙon abu ba ne don an haifi yaro da haƙori a bakinsa—in ji masana lafiyar yara

Likitocin kula da lafiyar yara sun ce jariran da ke da hakora daya ko biyu a lokacin haihuwa hakan ba baƙon al'amari ba ne. Wannan...