Sojoji sun mamaye kamfanin jaridar Daily Trust gida da waje

Daily Trust

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK / DAILY TRUST

Sojoji da jami’an tsaro na cikin gida DSS sun mamaye ofisoshin kamfanin jaridar Daily Trust a Abuja da Maiduguri.

A lokacin da wakilin BBC ya isa ofishin a Abuja, ya taras da sojojin da kuma wasu jami’an tsaro sanye da farin kaya sun zagaye ofishin inda suka hana shige da fice.

Mataimakin babban editan jaridar Mahmud Jega ya fada ma BBC cewa sojojin sun isa ofishin da kimanin karfe 4 na yamma, kuma sun kutsa ciki da karfe 5.33.

“Sojoji sun rufe ofishinmu na Maiduguri da safiyar yau, kuma sun tafi da wasu ma’aikatanmu biyu. A halin yanzu suna tsare da su a can”.

Daga nan sojojin sun bukaci dukkan ma’aikatan su taru a wuri guda kuma sun gudanar da bincike akan ma’aikatan da ke cikin ofis.

Binciken da wakilin BBC ya gabatar ya tabbatar da sojojin sun kai wa jaridar ta Daily Trust wannan samamen ne saboda babban labarin da ta wallafa yau Lahadi a shafinta na farko.

“Sun bukaci dukkan ma’aikatanmu su fice daga harabar ofishin, kuma sun kwace dukkan na’urorin aiki a hannun ma’aiakatan namu”, inji Mahmud Jega.

Har lokacin da ake hada wannan rahoton sojojin na cikin harabar ginin kuma sun kashe wutar ginin baki daya.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...