Sojoji sun mamaye kamfanin jaridar Daily Trust gida da waje

Daily Trust

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK / DAILY TRUST

Sojoji da jami’an tsaro na cikin gida DSS sun mamaye ofisoshin kamfanin jaridar Daily Trust a Abuja da Maiduguri.

A lokacin da wakilin BBC ya isa ofishin a Abuja, ya taras da sojojin da kuma wasu jami’an tsaro sanye da farin kaya sun zagaye ofishin inda suka hana shige da fice.

Mataimakin babban editan jaridar Mahmud Jega ya fada ma BBC cewa sojojin sun isa ofishin da kimanin karfe 4 na yamma, kuma sun kutsa ciki da karfe 5.33.

“Sojoji sun rufe ofishinmu na Maiduguri da safiyar yau, kuma sun tafi da wasu ma’aikatanmu biyu. A halin yanzu suna tsare da su a can”.

Daga nan sojojin sun bukaci dukkan ma’aikatan su taru a wuri guda kuma sun gudanar da bincike akan ma’aikatan da ke cikin ofis.

Binciken da wakilin BBC ya gabatar ya tabbatar da sojojin sun kai wa jaridar ta Daily Trust wannan samamen ne saboda babban labarin da ta wallafa yau Lahadi a shafinta na farko.

“Sun bukaci dukkan ma’aikatanmu su fice daga harabar ofishin, kuma sun kwace dukkan na’urorin aiki a hannun ma’aiakatan namu”, inji Mahmud Jega.

Har lokacin da ake hada wannan rahoton sojojin na cikin harabar ginin kuma sun kashe wutar ginin baki daya.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...