Sojoji sun kubutar da ‘yar bautar kasa daga wajen Boko Haram

Tun a watan Janairun wannan shekara ne aka sace ‘yar bautar kasan mai suna Halima Umar, a kan hanyar Goza zuwa garin Maiduguri. Wanda tun wancan lokacin babu ita ba duriyarta.

Rundunar sojin ta ce ta samu nasarar ceto matar ne sakamakon aikace-aikace da suke yi a dazuka, an dai mika matar ne ga gwamnatin jihar Borno.

Kwamandan rundunar sojin dake garin Maiduguri Birgediya Janar Bulama Biu, shine ya mika Halima ga mataimakin gwamnan jihar Borno Alhaji Umar Kadafur. Wanda kuma ya mika godiya da jinjina ga jami’an tsaron game da ayyuakan da suke gudanarwa a jihar.

More News

Ɗalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...