[ad_1]
Rundunar Sojan Nijeriya ta samu nasarar fatattakar wasu mayakan Boko Haram da suka kai wani mummunan hari a garin Jakana da ke karamar hukumar Kaga a jihar Borno.
Kwamandan rundunar shiyya ta bakwai, Birgediya Janar Bulama Biu ya ce mayakan sun shiga garin ne a jiya Alhamis da daddare dauke da manyan makamai amma kuma sojojin da ke garin sun samu nasarar fatattakarsu.
[ad_2]