Sojoji Sun Ceto Mutane 50 da Shanu 32 Bayan Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga a Katsina

Rundunar sojoji da ke karkashin aikin Operation FANSAN YANMA ta yi nasarar kubutar da mutane 50 da kuma kwato shanu 32 da aka sace, bayan sun dakile wani hari da ‘yan bindiga suka kai a kauyen Raudama, karamar hukumar Faskari, Jihar Katsina.

Majiyoyi sun shaida wa Zagazola Makama cewa harin ya faru ne da misalin karfe 8 na dare a ranar 27 ga Afrilu, 2025, lokacin da wasu ‘yan bindiga dauke da makamai suka kai hari kan al’ummar garin.

Dakarun soji da na ‘yan sanda suka yi gaggawar tura jami’an sintiri zuwa yankin, inda suka gwabza da maharan cikin tsananin artabu. A karshe, jami’an tsaro suka fi karfin ‘yan bindigar, wanda hakan ya tilasta musu yin gudu.

A yayin wannan aiki, duka mutane 50 da aka sace sun samu kubuta ba tare da rauni ba, sannan kuma an kwato dukkan shanun da aka sace.

Sai dai mutane biyu sun jikkata a yayin fafatawar. Wadanda suka jikkata su ne Mai’unguwa Isah Biredi, mai shekaru 50 da Hassan Na Sakaka, mai shekaru 40. An garzaya da su zuwa Asibitin Gwamnati na Funtua domin samun kulawa ta likitoci.

Hukumomi sun yaba wa jajircewar jami’an tsaro tare da kira ga al’umma da su ci gaba da baiwa hukumomin tsaro hadin kai domin kawo karshen matsalar ‘yan bindiga a yankin.

More from this stream

Recomended