Sojin Najeriya ne ke kawo tsaiko a yaki da Boko Haram – Buratai

Na’urarku na da matsalar sauraren sauti

Boko Haram ta kashe mutum 30 a Konduga ranar Lahadi. Akwai hotuna masu tayar da hankali

Hafsan sojojin kasa na Najeriya ya dora alhakin tsaikon da ake da ake samu a yakin da kasar ke yi da ta’addanci ga sojojin kasar da ke fagen daga.

Laftanar Janar Tukur Buratai ya zargi sojojin da rashin mayar da hankali domin kare kasar a dukkan ayyukan da umarce su da su yi, lamarin da ya ce abin takaici ne.

“Magana ta gaskiya ita ce za a iya alakanta duk wani koma-baya da muka samu a baya-bayan nan a ayyukan da muke yi da rashin mayar da hankali da nuna kaimi wurin bin umarnin da aka bayar ko ayyukan da aka tsara”.

A takaice za a iya alakanta hakan da rashin nuna halin ko-in-kula da dakarun da suke filin daga suke nunawa, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya ruwaito shi yana cewa a wurin wani taron ranar Talata.

Sai dai wani jami’in soji ya shaida wa BBC cewa kalaman na shugaban nasu “ba su da tushe, yana mai cewa idan ba a yaba musu ba, to bai kamata a tsine musu ba”.

Fiye da shekara 10 ke nan dakarun Najeriya na fafatawa da mayakan Boko Haram a arewa maso Gabashin kasar, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum sama da 30,000, yayin da wasu miliyoyi suka rasa muhallansu.

Janar Tukur Buratai ya shafe shekara hudu yana jagorantar rundunar sojin Najeriya

Manyan jami’an sojoji da kanana da dama sun rasa rayukansu a yakin, wanda gwamnati da sojoji suka ce sun ci karfinsa.

Sai dai har yanzu kungiyar na kai hare-hare, inda ko a ranar Lahadi sai da suka kashe mutum 30 a wani harin kunar bakin-wake, yayin da wasu 40 suka jikkata.

Masu sharhi na ganin irin wadannan kalamai na nuna gazawa ne daga bangaren shugabannin sojin, wadanda wasu da dama suke zarga da kasa yin katabus wuirn kawo karshen kungiyar ta Boko Haram duk da makudan kudaden da ake ware musu.

Baya ga Boko Haram, Najeriya na fuskantar matsalar ‘yan bindiga a arewa maso Yamma da masu satar mutane domin karbar kudin fansa a sassan kasar daban daban.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...