Shugabannin kungiyar ƙwadago za su tattauna da mambobinsu bayan ganawar da su ka yi da gwamnati.

Shugabannin kungiyoyin ƙwadago na NLC da TUC sun amince su tattauna da mambobinsu bayan ganawar da suka yi da tawagar gwamnatin tarayya a ranar Laraba kan yajin aikin da ake yi.

Taron ganawar ya gudana ne a ofishin mai bawa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu dake Abuja domin lalubo mafita kan yajin aikin.

Ma’aikatan sun tsunduma yajin aiki a ranar 14 ga watan Nuwamba domin nuna rashin amincewarsu kan yadda aka ci zarafin Joe Ajaero shugaban kungiyar kwadago ta NLC a jihar Imo.

Kungiyar ta yi zargin cewa kawo yanzu babu wanda aka kama ballantana gurfanar da su gaban kotu kan batun.

Sai dai a wata sanarwa da ya fitar kan yajin aikin mai bawa shugaban Æ™asar shawara kan sha’anin tsaro, Mallam Nuhu Ribadu ya ce tuni aka kama wasu da ake zargin suna da hannu kan lamarin.

Taron ganawar da aka yi ya samu halartar ministan Æ™wadago Simon Lalong da kuma karamar ninistar ma’aikatar, Nkeiruka Onyeajeocha.

Da yake magana bayan zaman da aka yi shugaban kungiyar TUC ya ce sun tattauna sosai da tawagar gwamnatin tarayya.

More News

An sake gano gawar wani shugaban Fulani da ya ɓata a jihar Filato

An gano gawar wani Arɗon Fulani, Umar Ibrahim da ya ɓace a cikin wata rijiya dake kauyen Jokom a ƙaramar hukumar Mangu ta...

An kama Æ´an kungiyar IPOB 18 da ake zargi da kisan Æ´an sanda

Rundunar yan sandan jihar Imo ta kama mutane 18 da ake zargi da zama yan kungiyar IPOB da suke da hannu a kisan Æ´an...

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da zaɓen gwamnan jihar Sokoto

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja ta tabbatar da zaɓen, Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto. Rukunin alkalan kotun su uku sun yi watsi da...

Kotun ɗaukaka ta soke zaɓen shugaban majalisar dokokin jihar Kaduna

Kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja, ta soke zaɓen kakakin majalisar dokokin jihar Kaduna, Yusuf Liman. Alkalan kotun uku sun bayar da umarni da a sake...