Shin ka san wane ne marigayi Justice Mamman Nasir?

FACEBOOK/AMINU GAMAWA

Hakkin mallakar hoto
FACEBOOK/AMINU GAMAWA

An haifi Justice Mamman Nasir a jihar Katsina a shekarar 1929.

Ya yi karatun sakandare dinsa a Kwalejin Kaduna inda ya samu takardar shaidar kammala karanun sakandare ta WAEC a 1947.

Daga bisani ya tafi jami’ar Ibadan inda ya samu digiri a harshen Latin.

Daga nan kuma ya tafi makarantar horar da lauyoyi inda ya samu digiri a bangaren shari’a a 1956 kuma a wannan shekarar ce aka rantsar da shi a matsayin cikakken lauya a wata kotu da ke Ingila da ake yi wa lakabi da ‘Licoln Inn.”

Ya dawo Najeriya a 1956 a matsayin lauya mai shigar da kara.

A 1961, an nada shi Ministan Shari’a na Arewacin Najeriya inda ya shafe shekaru biyar kan mukamin sai kuma daga baya ya zama darakta a ofishin lauyoyi masu shigar da kara na arewacin Najeriya a 1967.

A 1967 din dai Mamman Nasir ya zama babban lauya a ma’aikatar shari’a a jihar arewa ta tsakiya a wancan lokaci.

Ya rike wannan mukamin na shekaru bakwai inda daga nan ne aka nada shi alkalin kotun koli a 1975.

An kuma nada shi a matsayin shugaban kotun daukaka kara, mukamin da ya rike kenan har zuwa 1992 inda daga nan ne ya zama Galadiman Katsina.

An nada shi a matsayin Galadiman Katsina a ranar 9 ga watan Mayun 19992.

Ya kuma rasu ranar Asabar 13 ga watan Afrailun 2019.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...