An haifi Justice Mamman Nasir a jihar Katsina a shekarar 1929.
Ya yi karatun sakandare dinsa a Kwalejin Kaduna inda ya samu takardar shaidar kammala karanun sakandare ta WAEC a 1947.
Daga bisani ya tafi jami’ar Ibadan inda ya samu digiri a harshen Latin.
Daga nan kuma ya tafi makarantar horar da lauyoyi inda ya samu digiri a bangaren shari’a a 1956 kuma a wannan shekarar ce aka rantsar da shi a matsayin cikakken lauya a wata kotu da ke Ingila da ake yi wa lakabi da ‘Licoln Inn.”
Ya dawo Najeriya a 1956 a matsayin lauya mai shigar da kara.
A 1961, an nada shi Ministan Shari’a na Arewacin Najeriya inda ya shafe shekaru biyar kan mukamin sai kuma daga baya ya zama darakta a ofishin lauyoyi masu shigar da kara na arewacin Najeriya a 1967.
A 1967 din dai Mamman Nasir ya zama babban lauya a ma’aikatar shari’a a jihar arewa ta tsakiya a wancan lokaci.
Ya rike wannan mukamin na shekaru bakwai inda daga nan ne aka nada shi alkalin kotun koli a 1975.
An kuma nada shi a matsayin shugaban kotun daukaka kara, mukamin da ya rike kenan har zuwa 1992 inda daga nan ne ya zama Galadiman Katsina.
An nada shi a matsayin Galadiman Katsina a ranar 9 ga watan Mayun 19992.
Ya kuma rasu ranar Asabar 13 ga watan Afrailun 2019.