Ana ci gaba da samun rahotanni da ke cin karo da juna kan ikirarin da jami’an tsaro suke yi cewa sun tabbatar da tsaro a babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.
Babbar hanyar ta yi kaurin suna wajen sace-sace mutanen don neman kudin fansa, inda mahara suke cin karen su babu babbaka.
Kabiru Adamu wato wani masani kan harkokin tsaro a kasar ya ce an sace kimanin mutanen 200 a babbar hanyar a watanni hudu na farkon wannan shekarar.
Amma akwai wadanda suke ganin adadin mutanen ya wuce hakan.
Galibin matafiya da ke zirga-zirga a hanyar yanzu suna amfani ne da jirgin kasar ne, maimakon motoci da suka saba amafani da su a baya.
A makon da ya wuce ne jami’an tsaro a kasar suka ce sun tabbatar da tsaro a wannan babbar hanyar.
Wakilinmu Mukhtari Adamu Bawa ya kai ziyara babban tashar mota ta unguwar Jabi a Abuja don jin ta bakin wasu direbobi da fasinjoji kan ikirarin na jami’an tsaron.