Shin an samar da tsaro a hanyar Abuja zuwa Kaduna? – BBC Hausa

Sanda

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Ana ci gaba da samun rahotanni da ke cin karo da juna kan ikirarin da jami’an tsaro suke yi cewa sun tabbatar da tsaro a babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Babbar hanyar ta yi kaurin suna wajen sace-sace mutanen don neman kudin fansa, inda mahara suke cin karen su babu babbaka.

Kabiru Adamu wato wani masani kan harkokin tsaro a kasar ya ce an sace kimanin mutanen 200 a babbar hanyar a watanni hudu na farkon wannan shekarar.

Amma akwai wadanda suke ganin adadin mutanen ya wuce hakan.

Galibin matafiya da ke zirga-zirga a hanyar yanzu suna amfani ne da jirgin kasar ne, maimakon motoci da suka saba amafani da su a baya.

A makon da ya wuce ne jami’an tsaro a kasar suka ce sun tabbatar da tsaro a wannan babbar hanyar.

Wakilinmu Mukhtari Adamu Bawa ya kai ziyara babban tashar mota ta unguwar Jabi a Abuja don jin ta bakin wasu direbobi da fasinjoji kan ikirarin na jami’an tsaron.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...