Shin an samar da tsaro a hanyar Abuja zuwa Kaduna? – BBC Hausa

Sanda

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Ana ci gaba da samun rahotanni da ke cin karo da juna kan ikirarin da jami’an tsaro suke yi cewa sun tabbatar da tsaro a babbar hanyar Kaduna zuwa Abuja.

Babbar hanyar ta yi kaurin suna wajen sace-sace mutanen don neman kudin fansa, inda mahara suke cin karen su babu babbaka.

Kabiru Adamu wato wani masani kan harkokin tsaro a kasar ya ce an sace kimanin mutanen 200 a babbar hanyar a watanni hudu na farkon wannan shekarar.

Amma akwai wadanda suke ganin adadin mutanen ya wuce hakan.

Galibin matafiya da ke zirga-zirga a hanyar yanzu suna amfani ne da jirgin kasar ne, maimakon motoci da suka saba amafani da su a baya.

A makon da ya wuce ne jami’an tsaro a kasar suka ce sun tabbatar da tsaro a wannan babbar hanyar.

Wakilinmu Mukhtari Adamu Bawa ya kai ziyara babban tashar mota ta unguwar Jabi a Abuja don jin ta bakin wasu direbobi da fasinjoji kan ikirarin na jami’an tsaron.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...