Shehu Sani na son matar El-Rufai ta daina magana akan gashinsa

Shehu Sani, sanata dake wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya ya nemi gwamna Nasiru el-Rufa’i da jawa matarsa kunne kan yadda take yawan magana akan gashin kansa.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook sanatan ya ce matar gwamnan, Hadiza el-Rufai ko da yaushe tana magana akan gashin kansa a duk lokacin da ta fita yakin neman zabe.

Hadiza wacce mawallafiyar littafai ce ta kasance akan gaba-gaba wajen yakin neman zaben mijinta gabanin zaben gwamnan da za a gudanar ranar cikin watan Maris.

“Ina rokon Gwamna da ya gargadi matarsa da ta daina magana akan gashina a duk sa’ilin da taje yakin neman zabe.Duk inda taje maganar bata wuce ta gashina.Ba laifina bane idan mijinta bashi da arzikin gashi.Na dauki abin da take a matsayin kalaman batanci,zan kai kararta wurin Sheikh Gummi ko kuma majalisar Limamai. Haba jama’a,” a cewar sakon.

Wannan ne dai karo na farko da sanatan yayi musayan yawu da matar gwamnan.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...