Shehu Sani na son matar El-Rufai ta daina magana akan gashinsa

Shehu Sani, sanata dake wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya ya nemi gwamna Nasiru el-Rufa’i da jawa matarsa kunne kan yadda take yawan magana akan gashin kansa.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook sanatan ya ce matar gwamnan, Hadiza el-Rufai ko da yaushe tana magana akan gashin kansa a duk lokacin da ta fita yakin neman zabe.

Hadiza wacce mawallafiyar littafai ce ta kasance akan gaba-gaba wajen yakin neman zaben mijinta gabanin zaben gwamnan da za a gudanar ranar cikin watan Maris.

“Ina rokon Gwamna da ya gargadi matarsa da ta daina magana akan gashina a duk sa’ilin da taje yakin neman zabe.Duk inda taje maganar bata wuce ta gashina.Ba laifina bane idan mijinta bashi da arzikin gashi.Na dauki abin da take a matsayin kalaman batanci,zan kai kararta wurin Sheikh Gummi ko kuma majalisar Limamai. Haba jama’a,” a cewar sakon.

Wannan ne dai karo na farko da sanatan yayi musayan yawu da matar gwamnan.

More News

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...

Delta: An dawo da gawarwakin sojojin da aka kashe Abuja don yi musu jana’iza

Gawarwakin sojojin da aka kashe a jihar Delta kwanan nan sun isa maƙabartar sojoji ta kasa da ke Abuja. Gawarwakin sun iso ne da misalin...