Shehu Sani, sanata dake wakiltar mazabar Kaduna ta tsakiya ya nemi gwamna Nasiru el-Rufa’i da jawa matarsa kunne kan yadda take yawan magana akan gashin kansa.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook sanatan ya ce matar gwamnan, Hadiza el-Rufai ko da yaushe tana magana akan gashin kansa a duk lokacin da ta fita yakin neman zabe.
Hadiza wacce mawallafiyar littafai ce ta kasance akan gaba-gaba wajen yakin neman zaben mijinta gabanin zaben gwamnan da za a gudanar ranar cikin watan Maris.
“Ina rokon Gwamna da ya gargadi matarsa da ta daina magana akan gashina a duk sa’ilin da taje yakin neman zabe.Duk inda taje maganar bata wuce ta gashina.Ba laifina bane idan mijinta bashi da arzikin gashi.Na dauki abin da take a matsayin kalaman batanci,zan kai kararta wurin Sheikh Gummi ko kuma majalisar Limamai. Haba jama’a,” a cewar sakon.
Wannan ne dai karo na farko da sanatan yayi musayan yawu da matar gwamnan.