Senator Abbo: An gurfanar da sanatan da ya doki mace a gaban kotu | BBC Hausa

Sanata Abbo

Hakkin mallakar hoto
Senator Abbo

Sanatan nan na Najeriya wanda aka gani a wani bidiyo yana dukan wata mai tsaron shagon kayan jima’i ya gurfana a gaban kotu.

Sanata Elisha Abbo ya shaida wa BBC cewa shi ne a cikin bidiyon da aka yi ta bzawa amma kuma ya ce an goge bangaren da matar ita ma take bugun sa.

Kwamishinan ‘yan sandan birnin Abuja, Bala Ciroma ya shaida wa BBC cewa an gurfanar da sanatan amma kuma bai fadi abubuwan da ake tuhumar sanatan da su ba.

Jaridar Intanet ta Premium Times, wadda ta fara sakin bidiyon, ta rawaito mai magana da yawun ‘yan sanda, Anjuguri Manzah, cewa “‘yan sanda sun shigar da shari’a ne bayan sun ga irin halayyar sanatan a bidiyon”.

A ranar Larabar da ta gabata ne sanata Abbo ya yi kuka tare da neman afuwa kan abin da ya aikata, a wani taron manema labarai, kwana guda bayan da ‘yan sanda suka ce sun fara bincike.

An samu wasu rahotanni da ke nuna an tsare sanatan a ranar Alhamis, amma an bayar da belinsa washe gari Juma’a.

  • Ba halina ba ne ku yafe min – Sanata Abbo
  • Elisha Abbo: Atiku ya sa baki kan batun cin zarafin wata mata

Dan takarar shugabancin Najeriya na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar ya tofa albarkacin bakinsa a kan ce-ce-ku-cen da ya biyo bayan bidiyon nan da ya karade shafukan sada zumunta wanda ke nuna yadda sanata Abbo ya make matar.

Alhaji Atiku Abubakar ya ce ya yi wa sanatan farin sani amma kamata ya yi matasan shugabanni irinsa su zama abin koyi.

A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter, Atiku ya kara da cewa ya kamata sanatan ya mika kansa ga ‘yan sanda.

“Ina shawartarsa da ya fito fili ya nemi afuwa sannan ya mika kansa ga ‘yan sanda domin ya nuna dattako,” Atiku ya fada.

A wani sakon daban kuma, ya ce ya kamata jam’iyyar PDP ta dauki matakin ladaftarwa a kan sanatan.

“Ina kira ga uwar jam’iyyarmu ta PDP da ta dauki matakin ladaftarwa a kansa, su ma ‘yan sanda su tabbatar cewa doka ta yi aikinta.”

Sanata Elisha Abbo dai yana wakiltar mazabar Adamawa ta Arewa ne a majalisar dattawa, kuma wannnan shi ne karon farko da ya je majalisar.

Sanatan mai shekara 41 yana cikin ‘yan majalisar dattawa mafi kankantar shekaru a majalisar.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Wani mutumi ya kashe mahaifiyarsa a kan kudi

Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Osun sun kama wani mazaunin kauyen Kajola da ke kusa da Apomu a jihar mai suna Lukman Adejoju bisa...

Mayaƙan Boko Haram Biyu Sun Miƙa Kansu Ga Sojoji

Rundunar dakarun soja ta ƙasa da ƙasa wato Multi National Task Force(MNJTF) a turance shiya ta 3 dake Monguno a Najeriya ta bayar da...

Sojoji a birnin Ibadan  sun kama Æ´an fafutukar kafa Æ™asar Oduduwa

Dakarun rundunar sojan Najeriya  sun samu nasarar kama wasu mutane masu fafutukar kafa ƙasar Oduduwa a birnin Ibadan na jihar Oyo. Masu fafutukar sanye da...