Saraki ya yaba wa shugaba Buhari bayan ceto Zainab Aliyu

Bukola Saraki, Shugaban majalisar dattawa, ya yaba da kokarin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi ta fannin diflomasiyya wurin ganin an sako Zainab Aliyu da Ibrahim Abubakar daga gidan yarin kasar Saudiyya, bisa zargin da ake musu na shiga da miyagun kwayoyi kasar.

Mista Saraki, wanda ya yi yabon na shi a lokacin da Sanata Kabiru Gaya ya ta so da zancen a majalisa ranar Talata, ya ce sakin su ba karamin sauki ba ne ga ‘yan Najeriya.
Saraki ya yabawa shugaba Buhari da namijin kokarin da ya yi wurin ceto rayuwar Zainab Aliyu

Zainab Aliyu wacce ta ke daliba ce a Jami’ar Maitama Sule, da ke Kano, da kuma Ibrahim Abubakar, an kama su ne a kasar Saudiyya, bisa zargin shiga kasar da miyagun kwayoyi, inda aka kamata a filin tashi da saukar jiragen sama na Prince Mohammed Bin Abdulaziz da ke Madina, saboda an gano kwayar a cikin jakarta.

Zainab, ta yi yunkurin kare kanta, inda ta bayyana cewa saka mata kwayar aka yi a cikin jakarta.
Bugu da kari, an kama Abubakar shi ma a kasar da laifin shiga da kwaya.

Yayin da yake magana akan doka ta 43 ta majalisar dattijai, Mista Gaya ya ce ya kamata a yabawa shugaban kasa Muhammadu Buhari, Majalisar Dattijai, da duk wadanda suka ba da gudummawa wajen sakin su.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya ya ruwaito cewa Sakataren Ma’aikatar Harkokin Waje, Mustapha Sulaiman, wanda ya tabbatar da sakin su, ya ce an sake sune sakamakon an bi hanya ta diflomasiyya tsakanin gwamnatin Najeriya da ta Saudiyya.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...