Sambo Dasuki bai mutu ba, inji DSS

Hukumar tsaro ta farin kaya, DSS, ta tabbatar da cewa labarin da ake ta yadawa cewa tsohon mai bai shugaban kasa shawara kan sha’anin tsaro Kanal Sambo Dasuki ya rasu karya ne.

Kakakin hukumar Peter Afunanya ya shaida wa kafar talabijin ta kasa NTA cewa labarin karya ne ake yada wa, yana mai cewa “ba wai yana raye ba ne kawai, yana kuma cikin koshin lafiya.”

Ya kuma yi Allah wadai da labarin wanda ake ta yadawa a intanet, tare da yin kira ga jama’a su yi watsi da shi.

Sambo Dasuki ya shafe fiye da shekaru uku a tsare. Tun watan Disamban 2015 hukumar DSS ke tsare da shi kan zargin wawushe kudin da aka ware domin sayo makaman yaki da Boko Haram.

Ana ci gaba da tsare Dasuki ne duk da kotun Tarayya ta sha ba da shi beli, har da kotun ECOWAS.

Gwamnatin Buhari dai ta dade tana cewa tana ci gaba da rike shi ne saboda ta daukaka kara.

‘Yan jaridar da suka ziyarci inda ake tsare da shi sun ce sun yi tozali da shi, inda suka jima suna hira har ya amince aka dauki hotonsa domin karyata labarin ya mutu.

More News

APC ta dakatar da Ganduje a matakin gunduma

Mambobin jam'iyyar APC a mazabar da ke Karamar Hukumar Dawakin Tofa a Jihar Kano sun dakatar da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa Abdullahi Ganduje. ...

Yadda rikici a kan gishirin N20 ya yi sanadiyyar mutuwar wani mutum a Kano

Wani magidanci mai suna Zakari Hamza mai shekaru 45, ya gamu da ajalinsa a hannun kanen matarsa, wani Magaji Salisu saboda gishirin N20. Dan marigayin,...

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan IPOB 5

Dakarun rundunar sojan Najeriya da kuma ta rundunar sojan ruwan Najeriya a ranar Talata sun kashe mayaƙan ƙungiyar IPOB guda biyar a yayin musayar...

Ɗan agajin Izala ya samu lambar yabo, kujerar hajji, kyautar mota bayan ya tsinci naira miliyan 100 ya mayar wa mai su

Salihu AbdulHadi Kankia, mamba ne na kungiyar agaji ta kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Iqamatus Sunnah (JIBWIS), ya samu yabo da tukuicin mayar da...