Rundunar F-SARS Ta Koma Karkashin Jihohi

Rundunar wacce tsohon Sufeto Janar Ibrahim Idriss ya samar kuma ke karbar umarni daga hedikwata a Abuja ta yi kaurin suna wajen take hakkin dan Adam.

Kafin yanzu dai F-SARS na karbar umarni ne daga hedkwatar rundunar ‘yan sandan kasar, da a baya har zangar zangar lumana ‘yan Najeriya suka yi don neman a soketa, bisa zargin cin zarafin jama’a, al’amarin da yasa mataimakin shugaban kasar Farfesa Yemi Osinbsjo lokacin da yake rikon mukamin shugabancin kasar ya bada umarnin ayi mata gyaran fuska.

Daga yanzu dai an soke wannan bangare na ‘yan sanda a matakin tarayya don haka an maidasu karkashin kwamishinonin ‘yan sanda na jihohi.

Sufeto janar na ‘yan sandan ya yi gargadin cewa duk wani cin zali, sakaci ko ganganci da aka samu wannan runduna da aikatawa to za a dora alhakin hakan ne a wuyan kwamishinan ‘yan sandan da hakan ya faru a jiharsa ne.

Tuni dai masu fafutuka irin su Barrister Yakubu Sale Bawa suka yi marahaba da wannan mataki, inda suka bayyanashi da cewa zai taimaka wajen rage cin mutuncin jama’a da ake yi.

More News

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma’aikatar kudin jihar ta miÆ™ata bayanan bashin da El-Rufai ya ciwo

Majalisar dokokin jihar Kaduna ta nemi ma'aikatar kudi ta jihar da ta miƙa mata cikakken bayani kan basukan  da gwamnatin tsohon gwamnan jihar, Nasiru...

An dakatar da ayyukan kamfanin jiragen sama na Dana Air

Festus Keyamo, ministan harkokin sufurin jiragen sama ya umarci hukumar FAAN dake lura da sufurin jiragen sama a Najeriya ta dakatar da ayyukan kamfanin...

Yahaya Bello Ya Bayyana Dalilan Da Ya Hana Shi Bayyana A Gaban Kotu

Tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya ce tsoron kamun  hukumar EFCC dake yaÆ™i da yiwa tattalin arzikin Æ™asa ne ya hana shi bayyana...

Ƴan sanda sun kama mutane biyu dake samarwa ƴan fashin daji makamai a jihar Kaduna

Rundunar Æ´an sandan jihar Kaduna ta ce tana tsare da wasu mutane biyu da ake zargi da safarar bindiga a jihar. A wata sanarwa ranar...