Real Madrid ta sayo Eder Militao

FC Porto

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Kungiyar Real Madrid, ta dauki mai tsaron baya na kulob din FC Porto, Eder Militao.

Dan wasan mai shekara 21, shi ne na farko da Zinedine Zidane ya saya, bayan da ya sake karbar aikin kocin Madrid.

A sanarwar da Real ta sanar a shafinta na Intanet ta ce ”Real Madrid ta cimma yarjejeniya daukar dan wasan FC Porto, Eder Militao”.

Dan kwallon na Brazil ya amince zai koma Spaniya kan shekara shida, zai kuma koma can ne idan an kammala wasannin bana.

Rahotanni na cewa kudin daukar dan kwallon Brazil din ya kai fam miliyan 43.5, ana sa ran yarjejeniyarsa da Real za ta kare a karshen watan Yunin 2025.

Militao ya fara buga tamaula a Sao Paulo daga nan ya koma FC Porto a watan Agustan 2018, ya kuma taimakawa kungiyar Portugal ta kai wasan daf da na kusa da na karshe a gasar Zakarun Turai ta bana.

Tuni aka fitar da Real Madrid a gasar kofin Zakarun Turai da kuma Copa del Rey, sannan tana ta uku a kan teburin La Liga da tazarar maki 12 tsakaninta da Barcelona ta daya.

More News

ÆŠalibai a Jami’ar Jos na zanga-zanga saboda rashin wuta da ruwa

Wasu daliban jami’ar Jos da ke jihar Filato a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da matsalar karancin ruwa da rashin...

MTN yana ƙoƙarin ƙara kuɗin kati da data a Najeriya

Katafaren kamfanin sadarwa na MTN na kokarin kara kudin katin waya da na data a Najeriya. Kamfanin sadarwa mafi girma a nahiyar Afirka ya ba...

Gwamnatin Kano Ta Rage ₦500,000 A Kuɗin Aikin Hajjin Bana

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya sanar da yiwa maniyatan Aikin Hajji da suka fito daga jihar kyautar ₦500,000 domin su cika kuɗin...

Ƴan bindiga sun sace wani limami a jihar Kogi

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da Quasim Musa babban limamin garin Iyara dake ƙaramar hukumar Ijumu ta jihar Kogi. Lamarin ya faru ne a ranar...