Real Madrid ta sayo Eder Militao

FC Porto

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Kungiyar Real Madrid, ta dauki mai tsaron baya na kulob din FC Porto, Eder Militao.

Dan wasan mai shekara 21, shi ne na farko da Zinedine Zidane ya saya, bayan da ya sake karbar aikin kocin Madrid.

A sanarwar da Real ta sanar a shafinta na Intanet ta ce ”Real Madrid ta cimma yarjejeniya daukar dan wasan FC Porto, Eder Militao”.

Dan kwallon na Brazil ya amince zai koma Spaniya kan shekara shida, zai kuma koma can ne idan an kammala wasannin bana.

Rahotanni na cewa kudin daukar dan kwallon Brazil din ya kai fam miliyan 43.5, ana sa ran yarjejeniyarsa da Real za ta kare a karshen watan Yunin 2025.

Militao ya fara buga tamaula a Sao Paulo daga nan ya koma FC Porto a watan Agustan 2018, ya kuma taimakawa kungiyar Portugal ta kai wasan daf da na kusa da na karshe a gasar Zakarun Turai ta bana.

Tuni aka fitar da Real Madrid a gasar kofin Zakarun Turai da kuma Copa del Rey, sannan tana ta uku a kan teburin La Liga da tazarar maki 12 tsakaninta da Barcelona ta daya.

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ćłan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...