Ofishin yakin neman zaben Buhari ya yi tir da dage zaben Najeriya

Buhari

Hakkin mallakar hoto
Twitter/@BashirAhmaad

Ofishin yakin neman zaben Shugaba Buhari ya yi allawadai da matakin hukumar zaben kasar, INEC, na dage manyan zabuka.

Hukumar zaben ta ce ta dage zaben shugaban kasa daga ranar 16 ga watan Fabrairu zuwa 23 ga watan na Fabrairu.

Kazalika za a gudanar da zaben gwamnoni ranar tara ga watan Maris maimakon ranar biyu ga watan na Maris.

Sai dai sanarwar da Mr Festus Keyamo, mai magana da yawun ofishin yakin neman zaben shugaban Najeriya ya fitar ta zargi INEC da hada baki da jam’iyyar hamayya ta PDP domin magudin zabe.

“Muna fatan INEC za ta zama ‘yar ba-ruwanmu a annan harka ta zabe domin kuwa jita-jitar da ake watsawa na cewa an dage zaben ne da hada bakin babbar jam’iyyar hamayya ta PDP, wacce da ma bata shirya shiga zaben ba,” in ji Mr Keyamo.

Masu sharhi dai na ganin dage zaben zai janyo wa hukumar zaben bakin jini da kuma sanya shakku a zukatan ‘yan Najeriya game da shirnta na gudanar da sahihin zabe.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...