Nijar ta samu tallafi maganin malaria daga Amurka

Sauro ne ke haddasa cutar malaria

Hakkin mallakar hoto
Getty Images

Gwamnatin Amurka ta tallafa wa jamhuriyar Nijar da magungunan zazzabin cizon sauro wato malaria na milyoyin CFA.

Tallafin dai ya hada da magungunan rigakafin zazzabin cizon sauro dama na magance cutar da zarar an kamu da ita.

Kazalika daga cikin tallafin da Amurkan ta ba wa Nijar, akwai gidajen sauro.

Amurka dai ta bayar da wannan taimako ne ga Nijar da zimmar rage yaduwar cutar ta malaria da akshi 50 cikin 100.

Wannan tallafi na Amurkan, na daga cikin wani tsari ne na kasar wajen tallafa wa kasashe masu tasowa.

Cutar zazzabin cizon sauro na daga cikin cututtukan da ke saurin kisan kananan yara da ma mata masu juna biyu a kasar.

Gwamnatin Nijar ta kasa yakin da take a kan yaduwar cutar zuwa gida uku da suka hada da neman tallafi da wadatar da al’ummar kasar da maganin rigakafin cutar da kuma tsaftace unguwanni.

Kasashen Afrika ne suka fi fama da cutar zazzabin cizon sauro, kuma yawancin wadanda ke mutuwa yara ne.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...