Nijar ta kama wasu mafarauta guda uku ‘yan Najeriya da ake zargi da satar damun daji a daya daga cikin gandun dajin duniya da ke yammacin Afirka.
An kama su ne a kudu maso yammacin Dosso cikin motar daukar kaya guda biyu shake da hauren giwa da fatun maciji da kan wasu namun dawa da dama da suka kunshi na Bauna da Birai, kamar yadda kamfanin dillacin labaran AFP ya ruwaito.
Ana zargin sun yi farautar namun dajin ne ne daga wani babban gandun daji da ya hada kan iyakar Nijar da Burkina Faso da Benin.
Gwamnatin Nijar ta ce ta kuma kama bindigogin farauta da dama, da wasu sinadarai da mafarautan ke dauke da su.
Gandun dajin na Majalisar Dinkin Duniya na da girma sosai wanda kuma ke kunshe damun daji da dama.