Najeriya ta gargadi ƴan ƙasarta game da zuwa Nijar

Kwanturolan hukumar shige da fice ta Najeriya (NIS) mai kula da rundunar Jibia ta musamman a jihar Katsina, Mustapha Sani, ya gargadi ‘yan Najeriya kan yin balaguro zuwa Jamhuriyar Nijar.

Hakan dai ya zo ne sakamakon rikicin jamhuriyar Nijar bayan juyin mulkin da aka yi a kasar.

Kasar ta Afirka ta Yamma ta fuskanci takunkumi sakamakon kasancewerta karkashin mulkin soja.

Ya yi wannan jawabi ne a ranar Alhamis a wani bikin hadin gwiwa da hukumar NIS ta jihar Katsina domin bikin cika shekaru sittin.

More from this stream

Recomended