Najeriya Ta Bi Sahun Kasashen Da Suka Datakar Da Amfani Da Jirgin Boeing

Najeriya ma ta bi sahun sauran kasashen da suka dauki matakan dakatar da amfani da jirgin Boeing bayan hatsarin kasar Habasha Duk da cewa ba ta mallaki wannan nau’in jirgi na Boeing 737 Max 8 da 9 a kasar ba.

Ministan Ma’aikatar Sufurin jiragen sama a Najeriyar, Hadi Sirika, ya ce duk da cewa sararin samaniya mallakin duniya ne amma ya zama dole dauki wannan mataki.

“Da yake ka san cewa ita harkar sufurin jiragen sama, ta duniya ce bai daya, ba ta kasar Najeriya ba ce kawai, amma baayn an smau wannan hatsari a Habasha, abin da muka yi kokarin yi shi ne, duk jirgi samfurin wannan Boeing 737 Max 8 da 9, kar su ta shi kar kuma su sauka a Najeriya.”

Ya kara da cewa, “kuma cikin hukuncin Allah, babu wani da yake da irin wannan jirgi a Najeriya.” Sirika ya fada a wani taron manema labarai.

A jiya Laraba, shugaban Amurka Donald Trump, ya dakatar da amfani da nau’in jirgin saman samfurin Boeing da ake kerawa kasar.

“Amurka na da kyakkyawan tarihi idan ana magana akan matakan kiyayen hadurra a fannin zirga zirgar jiragen sama, muna kuma so tarihin ya dore, saboda haka, ba na so na yi sako-sako da wannan lamari.” Trump ya ce.

Wannan mataki da Amurkan ta dauka, shi ne mafi girma cikin jerin kasashen da ke daukan matakan dakatar da amfani da jirgin.

A baya bayan nan, China, Habasha, Turkiyya, Brazil, Korea ta Kudu da daukacin kasashen da ke tarayyar turai, sun dakatar amfani da jirgin na wani lokaci.

Kididdigai dai ta nuna cewa, kafin aukuwar wannan hadari na Ethiopia, akwai akalla nau’in wannan jirgi 400 da suke aiki a duk fadin duniya.

More News

EFCC na neman Yahaya Bello ruwa a jallo

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (Economic and Financial Crimes Commission) ta bayyana tsohon gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello a matsayin...

Mutane da dama sun mutu bayan motar fasinja ta taka bam a Borno

Akalla mutane 16 ne ake fargabar sun mutu yayin da wasu 20 suka jikkata bayan wata motar fasinja da ke kan titin Baga-Kukawa a...

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon ĆŠaya Daga Cikin Ćłan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon É—aya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...