Najeriya da Cuba za su ƙara ƙulla alaƙa mai ƙarfi

Mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima a ranar Alhamis ya bayyana bukatar gwamnatin shugaba Bola Tinubu na kara zurfafa dangantakar da ke tsakanin kasar Najeriya da Jamhuriyar Cuba.

Daraktan yada labarai na ofishin mataimakin shugaban kasar, Olusola Abiola, a cikin wata sanarwa da ya fitar, ya ce Shettima ya bayyana hakan ne yayin wata ziyarar ban girma da ya kai wa mataimakin shugaban kasar Cuba, Salvador Valdez Mesa a fadar De Revolution, Havana.

A halin yanzu Mista Shettima yana kasar Cuba ne domin wakiltar Tinubu a taron shugabannin kasashen G77+ na kasar Sin a birnin Havana na kasar Cuba, wanda ake gudanarwa daga ranar 15 zuwa 17 ga watan Satumba.

Ya kara da cewa, “Muna matukar girmama kasar Cuba, musamman irin sadaukarwar da kuka yi mana a Afirka.”

Yayin da yake yabawa da dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, Mista Shettima ya jaddada bukatar kasashen biyu su sake kulla alaka a nan gaba.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...