Mutum 78,000 ne suke mutuwa saboda cutar jeji duk shekara a Najeriya—ƙungiyar likitoci

Kungiyar Likitocin Radiation da Clinical Oncologists ta Najeriya (ARCON) ta ce aƙalla mutane 78,000 ne ke mutuwa sakamakon kamuwa da cutar daji a duk shekara a fadin tarayya.

Yayin da ta kuma nuna rashin jin dadin yadda ‘yan Najeriya ke da lafiyarsu, hukumar ta gabatar da cewa alkaluman da aka gudanar a halin yanzu sun nuna cewa kimanin mutane 125,000 ne ake samun rahoton bullar cutar a duk shekara a kansu a kasar.

Shugaban kungiyar, Dokta Amaka Lasebikan, wanda ya yi jawabi ga manema labarai jiya a Enugu, gabanin taronsu na kimiyya da za a fara daga yau, ya bayyana cewa, matsalar ciwon daji a Najeriya na karuwa, don haka akwai bukatar gwamnati, daidaikun mutane da masu bayar da lafiya su tashi tsaye don magance matsalar.

Ƙungiyar ta ɗaura laifin rashin daidaiton samun kulawar cutar kansa, wanda a cewarta, ya fallasa majinyata da dama ta fuskar bambance-bambancen zamantakewa da tattalin arziki.

More News

An samu ambaliyar ruwa a Adamawa

Anguwan Tana, al’ummar karamar hukumar Yola ta Arewa, sun shiga tasgaro a ranar Alhamis sakamakon ambaliya daga kogin Kilange da kogin Faro. Mazaunan garin...

Sojoji sun ceto mutane 6 daga cikin ɗaliban jami’ar Gusau da aka sace

Sojoji sun ceto dalibai mata shida daga cikin daliban Jami'ar Gwamnatin Tarayya dake Gusau da aka bada rahoton yan bindiga sun yi garkuwa da...

Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗaliban Jami’ar Tarayya da ke Gusau

An sace wasu daliban jami’ar tarayya ta Gusau da ba a tantance adadinsu ba da sanyin safiyar Juma’a. ‘Yan ta’addan masu yawan gaske sun...

Ƴan sanda sun kama masu safarar makamai wa ƴan bindiga

Jami’an hukumar ‘yan sanda reshen Karasuwa a jihar Yobe sun cafke wasu mutane biyu da ake zargi da kai wa ‘yan bindiga makamai da...