Mutane sama da 100 ne da suka hada da malaman manyan makarantu,yan siyasa da kuma kwararru ke hankoran darewa gurbin kujerar kwamishina a jihar Kano.
Jaridar Daily Trust ta gano cewa yan siyasar dake neman mukamin sun fito ne daga bangarorin siyasa daban-daban da suka hada da tsagin tsohon gwamna,Malam Ibrahim Shekarau, tsagin tsohon mataimakin gwamna, Farfesa Hafiz Abubakar da kuma tsagin tsohon shugaban hukumar lura da tashoshin jiragen ruwa ta Najeriya, Aminu Dabo.
Wata majiya dake kusa da gwamnatin ta fadawa jaridar cewa kaso 40 ne kacal cikin tsofaffin kwamishinonin ake sa ran za su sake dawowa kan mukamansu.
Majiyar da ta nemi a boye sunanta ta bayyana kaso 60 na tsofaffin kwamishinonin ba za su dawo ba bayan da suka gaza yin kokari a lokacin zangon farko na gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje.