Mutane sama 100 ne ke neman Ganduje ya nada su kwamishinoni

Mutane sama da 100 ne da suka hada da malaman manyan makarantu,yan siyasa da kuma kwararru ke hankoran darewa gurbin kujerar kwamishina a jihar Kano.

Jaridar Daily Trust ta gano cewa yan siyasar dake neman mukamin sun fito ne daga bangarorin siyasa daban-daban da suka hada da tsagin tsohon gwamna,Malam Ibrahim Shekarau, tsagin tsohon mataimakin gwamna, Farfesa Hafiz Abubakar da kuma tsagin tsohon shugaban hukumar lura da tashoshin jiragen ruwa ta Najeriya, Aminu Dabo.

Wata majiya dake kusa da gwamnatin ta fadawa jaridar cewa kaso 40 ne kacal cikin tsofaffin kwamishinonin ake sa ran za su sake dawowa kan mukamansu.

Majiyar da ta nemi a boye sunanta ta bayyana kaso 60 na tsofaffin kwamishinonin ba za su dawo ba bayan da suka gaza yin kokari a lokacin zangon farko na gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje.

More News

An kori sojojin Najeriya biyu saboda satar kebul a matatar Dangote

Rundunar sojin Najeriya ta tabbatar da korar wasu sojoji biyu da ake zargi da satar igiyoyin sulke a harabar matatar Dangote da ke jihar...

Magoya bayan APC da dama sun koma NNPP a Kano

Jam'iyar NNPP ta karɓi magoya bayan jam'iyar APC da dama a jihar Kano. Mataimakin gwamnan jihar Kano, Aminu Abdul Salam Gwarzo shi ne ya karɓi...

Sojoji sun gano masana’antar Æ™era bom a jihar Borno

Dakarun rundunar sojan Najeriya sun gano wata masana'anta da mayaƙan kungiyar ISWAP suke ƙera bama-bamai. Masana'antar ƙera bama-bamai an gano ta ne a Abulam-BUK dake...

Atiku ya ziyarci Abdul Ningi

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya ziyarci dakataccen ɗan majalisar dattawa sanata, Abdul Ningi dake wakiltar mazaɓar Bauchi ta tsakiya a majalisar dattawa. Atiku...