Mutane biyar sun mutu a hatsarin kwale-kwale da ya faru a jihar Lagos

[ad_1]








Aƙalla mutane biyar ne suka mutu a wani hatsarin kwale-kwale akan hanyarsu ta zuwa yankin Ikorudu a jihar Lagos.

Adesina Tiamiyu, shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Lagos LASEMA ya tabbatar da faruwar lamarin.

Ya ce hukumar ta samu kiran kai daukin gaggawa da misalin karfe 5:30 na yamma.

Tiamiyu ya ce wani jirgi mai cin mutane 20 mallakin kamfanin Blue Sea ya nutse a tsakiyar teku akan hanyarsa ta zuwa Ikorudu daga tsibirin da ake kira Lagos Island.

Binciken farko da aka gudanar bai nuna musabbabin faruwar hatsarin ba.

“Abin takaici mutane biyar (mata 4 da kuma namiji daya) aka tabbatar da mutuwarsu kuma tuni aka ajiye gawarwakinsu a dakin ajiye gawarwaki dake babban asibitin Ikorudu,”a cewar Tiamiyu.




[ad_2]

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...