Mutane 20 aka kashe a wani hari kan masallaci dake kauyen Kwaddi a jihar Zamfara

[ad_1]








Wasu daga ake zargin barayi ne sun kashe a kalla mutane 20 lokacin da suka kai wani hari kan kauyen Kwaddi dake karamar hukumar Zurmi ta jihar Zamfara.

Lamarin ya faru ne a wani masallaci lokacin da ake gudanar da sallar la’asar.

A makon da ya gabata akalla mutane 30 aka kashe a wani harin makamancin wannan da wasu yan bindiga suka kai a lardin Goga dake karamar hukumar Maradun ta jihar.

Kauyen Kwaddi na tsakiyar daji inda yake kewaye da duwatsu kuma yayi iyaka da jamhuriyar Nijar.

Tun da fari yan bindigar sun kashe mutane 8 a kauyen bayan da mutanen garin suka gaza biyan kuɗin fansa na miliyan ₦1 da suka bukaci a biya.

“Sun sake bayar da wa’adin biyan kudin fansar inda suka tafi.Yawancin mazauna kauyen kananan manoma ne babu ɗaya daga cikinsu dake iya tunkahon yana da ₦50,000.Sun dawo inda suka kai hari lokacin da mutane suke sallah,”a cewar wani mazaunin garin.

“Lokacin ana ruwan sama sun bar masallaci inda suka shiga bi gida-gida suna harbin mutane a gidajen su ciki har da wadanda suka tsira daga harin masallacin.”

Mai magana da yawun rundunar ƴansandan jihar, Muhammad Shehu ya tabbatar da faruwar lamarin.




[ad_2]

More News

Sojoji Sun Ceto Lydia Simon Ɗaya Daga Cikin Ƴan Matan Chibok

Dakarun sojan Najeriya dake aiki da rundunar samar da tsaro ta Operation Desert Sanity III sun samu nasarar ceto, Lydia Simon ɗaya daga cikin...

Gwamna da ƴansanda sun daƙile yunkurin EFCC na kama Yahaya Bello

A ranar Laraba ne Gwamnan Jihar Kogi, Usman Ododo, ya dakile wani yunkurin da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati ta...

Gwamnatin Tarayya Za Ta Fara Rabon Gidaje 8925

Gwamnatin tarayya ta ce ta fara raba gidaje 8925  ga mutanen da suka nema kuma suka cancanci a basu a faɗin ƙasa baki ɗaya...

Ƴan Bindiga A Zamfara Sun Kashe Sakataren Jam’iyar PDP

Wasu ƴan bindiga da ba a san ko suwaye ba sun kashe, Musa Ille  sakataren jam'iyar PDP na ƙaramar hukumar Tsafe a jihar Zamfara. Zagazola...